http://www.hausawglwpwzr4svrerazwxt7mqpcw3hfoxp5r7jjrkttqc3qrs5syid.onion/a/zaben-2023-kotu-ta-dage-zaman-sauraron-karar-jam-iyyar-labour-ta-kuma-yi-watsi-da-karar-jam-iyyar-app/7086950.html
Daya daga cikin lauyoyin dake kare zababben shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu a gaban kotun sauraron kararrakin zaben Dakta Hassan, mai mukamin SAN, yace da maraicen ranar Talata ne lauyan da ke kare jam’iyyar APP ya sanar da niyyar janye karar wadanda yake karewa kuma ya gabatar da matakin a gaban kotu, abinda ya sa alkalin kotun ya yi watsi da karar ta jam’iyyar APP.